Besiktas ta ki amincewa da tayin Ajax na daukar dan wasan Najeriya Wilfred Ndidi.
Besiktas taki amincewa da tayin Ajax na daukar dan wasan Najeriya Wilfred Ndidi.
2
ga Janairu, 2026
Daga
Usman Ibrahim.
kyakkyawan
salon wasa da ɗan wasan tsakiya Wilfred
Ndidi ya nuna a matakin kungiyarsa da ƙasarsa Najeriya ya ja hankalin
ƙungiyar kwallon kafa ta Ajax dake kasar Netherlands sai dai ƙungiyar Beşiktaş ta ƙi amincewa da tayin da
aka kawo mata.
Rahotanni
sun nuna cewa tayin da aka tattauna ya ƙunshi aro na Yuro Miliyan Biyu (€2m) tare da zaɓin saye na Yuro
Miliyan (€12m) amma Beşiktaş ba
ta shirya karɓar wannan tayin a wannan lokaci ba.
Ndidi
ya taka muhimmiyar rawa a tsakiya tare da baiwa tawagar Super Eagles gagarumin gudunmuwa a gasar cin kofin kasashen
Nahiyar Afirika wato AFCON na 2025
da aka kammala a kasar Morocco inda Najeriya ta kammala gasar a matsayi na uku
tare da lashe lambar tagulla.
Zaku
Iya bibiyarmu a kafafenmu kamar haka.
Facebook
YCMC News
You
Tube YCMC News
Tit
Tok YCMC News

Comments
Post a Comment