Yan Sanda sun ceto wasu Mutane da aka yi garkuwa da su a Jihar Kebbi.
Yan Sanda sun ceto wasu Mutane da aka yi garkuwa da su a Jihar Kebbi.
2
ga Janairu, 2026
Rundunar
’Yan Sandan Jihar Kebbi ta samu wata gagarumar nasara a yaƙin da take yi da
satar mutane da fashin daji, inda ta ceto mutane biyu da aka sace tare da cafke
wani wanda ake zargi, a yayin wasu aikin hadin gwiwa na magance matsalar tsaro
da aka gudanar a ƙananan hukumomin Kalgo da Dandi na jihar.
Da
yake tabbatar da faruwar lamarin, Jami’in Hulɗa da Jama’a na Rundunar ’Yan
Sandan Jihar Kebbi, SP Bashir Usman, ya ce aikin ya nuna ƙudirin rundunar na
hana masu aikata laifuka samun mafaka a cikin jihar.
Usman
ya ce an ceto mutanen ba tare da sun ji rauni ba, sakamakon daukin gaggawa da jami’an
tsaro da kuma kyakkyawar haɗin gwiwa da Ƙungiyar Sa-kai ta Vigilante Group suka
yi.
Ya
sake jaddada ƙudirin rundunar ’yan sandan jihar Kebbi na amfani da bayanan
sirri da kuma ɗaukar matakan kariya tun kafin aikata laifi, yana mai tabbatar
wa al’umma cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka domin tarwatsa cibiyoyin masu
satar mutane a faɗin jihar.
Rundunar
ta kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa hukumomin tsaro sahihan bayanai
akan lokaci, tana mai jaddada cewa haɗin kan al’umma na da matuƙar muhimmanci
wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a Jihar Kebbi.
Zaku
Iya bibiyarmu a kafafenmu kamar haka.
Facebook
YCMC News
You
Tube YCMC News
Tit
Tok YCMC News

Comments
Post a Comment