Posts

Showing posts from August, 2026

Young Spiders ta lashe Gasar cin kofin Zaman Lafiya na Gwamna Uba Sani

Image
Young Spiders Kasuwan Magani ta lashe Gasar cin kofin Zaman Lafiya na Gwamna Uba Sani. Daga Usman Ibrahim  9 ga watan Ogustan, 2026. Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Young Spiders ta Kasuwan Magani ta zama zakarar gasar cin kofin kwallon kafa na Gwamnan Uba Sani  da aka gudanar a Ƙaramar Hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna, bayan da ta doke Kufana United da ci 2–0 a wasan ƙarshe. An gudanar da wasan ƙarshen ne a filin wasa na Kajuru Township Stadium, inda dimbin masoya ƙwallon ƙafa, shugabannin al'umma, jami'an gwamnati da sauran manyan baƙi daga ciki da wajen ƙaramar hukumar suka halarta. Mataimakin Shugaban Ƙaramar Hukumar Kajuru, Muhammad Shuaibu, ne ya shirya gasar da nufin inganta zaman lafiya, haɗin kai da fahimtar juna tsakanin al'ummomi daban-daban na yankin, tare da nuna goyon baya ga gwamnatin Gwamna Uba Sani.    Young Spiders ce ta fara samun damar cin ƙwallo, inda Sagiru Gambo ya buɗe ƙwallon a minti na 12, bayan da ya samu damar zura ƙwallon a raga. Ana tsaka da wasa...

Hon. Dauda Madaki ya Jaddada Aniyar Gwamnatin sa wajen Inganta tsarin Shugabanci ta hanyar anfani da Sahihan Bayanai.

Image
  HON. DAUDA MADAKI YA JADDADA ANIYAR GWAMNATINSA NA INGANTA TSARIN SHUGABANCI TA HANYAR AMFANI DA SAHIHAN BAYANAI. Daga, Usman Ibrahim Mahuta. 5 ga watan Ogustan, 2026. Shugaban Majalisar Ƙaramar Hukumar Kajuru, Honorable Dauda Madaki ya bayyana cewa gwamnatin sa zata ci gaba da barin kofarta a bude wajen gudanar da harkokin Shugabanci ga Al'umma don ci gaba. Dauda Madaki ya bayyana haka ne a cikin wata Sanarwa data samu Sanya hannun Sakataren yada labaran sa, Mr. John Ezra Sojah. Hukumar kula da kasafi da tsare-tsare ta Jihar kaduna tare da hadin gwiwar Hukumar UNICEF Ofishin kaduna ne suka shirya taron karawar Juna sanin na kwanaki Uku ga Shugabannin kananan Hukumomin Jihar kaduna a taron daya gudana a Jihar Kano. A cewar Sanarwar, Dauda Madaki ya sake tabbatar da aniyar gwamnatin sa na ci gaba da haɗin gwiwa da Gwamnatin Jihar Kaduna da UNICEF da sauran abokan hulɗar domin ƙarfafa ƙwarewar hukumomi, bunƙasa shugabanci mai haɗa kowa da kowa, da aiwatar da shirye-shiryen da za su...