Shugaban NFF ya Bukaci a Daina Cunkusa Kalandar wasannin Premier ta Najeriya
Daga Usman Ibrahim...
Gabanin Gasar kwararru ta kasa wato Nigeria premier league na kamar wasa ta 2024/2025, shugaban Hukumar kwallon kafa ta Kasa, Alhaji Ibrahim Musa Gusau, ya bukaci Kwamitin shirya gasar daya daina Sanya wasannin da zasu Cunkushe wanda zai ci karo ko haifar da tarharo a lokacin gasar.
Gusau ya bayyana hake ne yayin da Yake Jawabi a lokacin Babban Taron hukumar daya gudana a Abuja inda ya jaddada cewa a shirye suke wajen ganin gasar ya samu Gagarumin ci gaba .
Ana saran Fara gasar Nigeria premier league ne a ranar Asabar 31 ga watan Ogustan 2024, inda masu Rike da Kambun gasar Rangers International zata kara da El-Kanemi Warriors a wasan Farko na Gasar.
YCMC MEDIA.

Comments
Post a Comment