Allah ya yiwa Sheik Shehu Usman Rigi-Rigi rasuwa



2 ga Janairu, 2026

Labari daga Abubakar Dan Yaro

Innalillahi wainnailaihirrajiun:

Allah ya yiwa Fitacccen Malamin Addinin Musulunci nan a Jihar Kaduna, Sheik Shehu Usman Idriss wanda aka fi Sani da Regi-regi na Manzon Allah.

Kafin rasuwarsa Malamin ya shahara Wajen sanya mabiyansa da Sauran Al'ummar Musulmai nishadi Saboda salon wa'azinsa.

Shiek Shehu Usman ya rasu ya bar Matansa 4 da yara 37 da jikoki da dama 

Za'a gudanar da Jana'izarsa da Karfe 4:30pm na yammacin yau idan Allah ya kaimu a Gidansa dake Kusfa Zaria.

Da Fatan Allah ya gafarta Masa da Rahama Amin.


Comments

Popular posts from this blog

Kaduna Polytechnic tayi cikakken bayani akan jinkirin Kiran dalibai da suka Kammala karatu zuwa aikin yiwa Kasa hidima.

Besiktas ta ki amincewa da tayin Ajax na daukar dan wasan Najeriya Wilfred Ndidi.

Yan Sanda sun ceto wasu Mutane da aka yi garkuwa da su a Jihar Kebbi.