Rundunar sojin Najeriya ta kashe mataimakin shugaban Boko Haram a Jihar Borno

 




Rundunar soji ta kashe mataimakin shugaban Boko Haram

 

2 ga Janairu, 2026

Daga Usman Ibrahim

 

Dakarun Operation Hadin Kai sun kashe wani babban jagoran Boko Haram, wanda aka bayyana shi a matsayin mataimaki na biyu tare da wasu mayaka goma a Dajin Sambisa da ke Jihar Borno.

An bada rahoton cewa an kashe ‘yan ta’addan ne a yankin Komala da ke Ƙaramar Hukumar Konduga yayin wani samame da rundunar ta kai da daddare.

A cikin wata sanarwa da Jami’in Yaɗa Labarai na rundunar,

Laftanar Kanal Sanni Uba ya fitar, ta ce an kuma kwato makamai da dama daga hannun yan ta’addan.

Ya ce lamarin ya faru ne sa’o’i 24 bayan da sojoji suka hallaka fitaccen kwamandan Boko Haram da ISWAP, Julaibib a yankin Gujba na Timbuktu Triangle.

Ya ƙara da cewa an kwato bindigogi kirar AK-47 guda biyar da harsasai da kekuna da kayayyakin abinci da kuma magunguna masu yawan gaske.

Zaku Iya bibiyarmu a kafafenmu kamar haka.

Facebook YCMC News

You Tube YCMC News

Tit Tok YCMC News

 


Comments

Popular posts from this blog

Kaduna Polytechnic tayi cikakken bayani akan jinkirin Kiran dalibai da suka Kammala karatu zuwa aikin yiwa Kasa hidima.

Besiktas ta ki amincewa da tayin Ajax na daukar dan wasan Najeriya Wilfred Ndidi.

Yan Sanda sun ceto wasu Mutane da aka yi garkuwa da su a Jihar Kebbi.