Posts

Gwamna Zulum ya baiwa Manoma Tallafi a Damasak.

Image
Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar  Borno yayi alkawarin rage irin radadi na halin da alumma musanman manoma suka shiga sakamakon cire tallafin man fetur a Damasak shalkwatar karamar hukumar Mobbar ta jihar domin bunkasa tsarin samar da wadataccen Abinci a jihar. Garin Damasak, daya ne daga cikin yankunan da jihar Borno ke alfahari dashi wajen samar da abinci, yankin sannu a hankali yana farfadowa bayan kwashe tsawon shekaru Suna cikin matsala sakamakon Rikicin kungiyar Boko Haram. Gwamnan na magana ne lokacin da yake ziyarar aiki na kwana biyu domin duba yadda ake raba kayan tallafi ga matan da suka rasa mazajen su da mata masu karamin karfi, ya kuma yi Alkawarin maida jihar Borno cikin jihohin da suka fita daga duk wata matsala ta karancin abinci a kasarnan. Ya kuma sha alwashin basu gudunmuwar Injin ban ruwa mai anfani da hasken Rana da iri na shuka da takin zamani a dai sauran kayayyakin aikin gona don ci gaban jihar. Daga Abubakar Abdullahi. Labaran YCMC media Kaduna.

Gamayyar kungiyoyin Arewa Sun koka akan tsadar kayan Masarufi

Image
  Talata 6-2-2024 7:00pm Gamayyar kungiyoyin Arewacin Najeriya Sun bayyana damuwarsu akan yadda kayayyakin masarufi ke ci gaba da tashin gwauron zabi a fadin Kasarnan. Jaridar Daily Trust ta bada Rahoton cewa,  yan Najeriya daban daban suna ci gaba da nuna Damuwa da fargaba a sakamakon halin kunci da suke ciki sakamakon hauhawar farashin kayayyaki. Kamar su Shinkafa da Filawa da Siga da Siminti da dai sauransu kuma an danganta lamarin akan yadda farashin Naira ke ci gaba da faduwa a kasuwan cinikayyar kudi wanda hakan yasa alumma basa iya rayuwa cikin Natsuwa da wadata. A cikin wata Sanararwa da Shugaban Gamayyar kungiyar na kasa , Jamilu Aliyu Charanchi, ya fitar ya ce  lamarin ya kai yan Najeriya ga Bango matuka wanda ke bukatar a dauki kwararan matakai da suka da ce. Labaran YCMC media Kaduna.

Anyi Kiran Sanya Dokar ta Baci a bangaren Abinci a Najeriya

Image
Talata 6-2-2024. 7:00pm Kungiyar yan jarida masu rajin tabbatar da Zaman lafiya a jihar kaduna (NPJK) ta bukaci a Sanya dokar ta baci a bangaren samar da issshen abinci a fadin kasarnan. Ta Bukaci Gwamnatin tarayya Dana jihohi su dauki kwararan matakan da suka dace don saukakawa alumma halin kunci da suke ciki yanzu haka na matsin Rayuwa. Mallam Ibrahim Yakubu, shine Shugaban tawagar ta NPJK, ya bayyna wasu dalilai daya sa alumma suke fama da wahala musanman Mata da kananan yara wanda ya hada da tashin farashin man fetur da cire tallafin mai wanda ke matukar yin illa ga rayuwar yan Najeriya. Yayi kira da a dauki matakan da suka dace don kawo mafita ga wannan hali da ake ciki, yayin da ya bukaci Gwamnatocin jihohi su tattauna da Shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu don sanya dokar ta baci a bangaren samar da binci isasshe a Najeriya. Labaran YCMC media Kaduna.

Abubakar Signed five year deal with F c Gent of Belgium

Image
Nigeria's Golden Eaglets striker Abubakar Abdullahi Idris has signed a four and half year contract with Belgium Club side F c Gent. A top source From his Manager, revealed that the youngster, who made a name for himself with his brace in the final of the WAFU B AFCON qualifying tournament in Ghana is expected to make another name in Belgium. The Kaduna based Footballer, Abubakar Abdullahi who joined Gent from Jega United of Kebbi State Nigeria, has perform well in the club program before his signing  with the Belgium Club side. Speaking after the signing, Abubakar thanked his parents, guidance and his Managers and those that supported him towards his success and urged them to continue to pray for him. YCMC MEDIA.

Tawagar Arewa maso gabas ta lashe gasar YSFON Na kasa Bayan doke Arewa maso yamma a wasan karshe

Image
 Tawagar kwallon kafa ta YSFON Na shiyyar Arewa Maso gabas ta lashe gasar YSFON U-16 na kasa Da aka kammala a jihar Kaduna Bayan doke shiyyar Arewa Maso yamma daci Daya mai ban haushi a wasan karshe. Wasan karshen Wanda ya gudana a filin wasa Na Ahmadu Bello Dake nan Kaduna ya Samu halartar manyan baki Da suka fito Daga bangarori daban daban Da sauran yan kallo Da suka fito Domin Shaida gasar na kasa. Dan wasan Arewa maso gabas Abdulrahman Ali shine ya zura kwallo guda data makale tun kafin aje Hutun Rabin lokaci Na wasan a gaban Yan kallo musanman magoya bayan shiyyar Arewa Maso yamma. Tawagar Arewa Maso yamma ta rinka matsa lamba wa tawagar Arewa maso gabas Dan ganin ta Rama kwallon Amma kokari Da jajurewa Na mai tsaran raga Na tawagar Arewa maso gabas Adamu Ibrahim yasa an gaza Rama kwallon Kuma tawagar Arewa maso gabas ce ta lashe gasar. Da yake jawabi Bayan Mika kofin GA Wanda suka lashe, Kwantrola na hukumar shige Da fice ta kasa reshen jihar Kaduna,Bashir Muhammad Lawal ya ...

Northeast YSFON team beat Northwest to emerged Champions at the just Concluded National U-16 Football Championship Kaduna

Image
YSFON northeast Football team has emerged Champions at the just Concluded YSFON National U-16 Football Championship Kaduna after beating Northwest YSFON team by a lone goal in the final match. The final match which took place at the main bowl of the Ahmadu Bello Stadium Kaduna witnessed lot of dignitaries from various sectors and spectators who came to witnessed the National event. Abdulrahman Ali scored the only goal for the Northeast Team in the first half of the game in front of Northwest supporters. The Northwest Team have been putting pressure on the Northeast Team to ensure they equalise the goal but unfortunately with the brilliant performance of northeast goal keeper Adamu Ibrahim did not give any room for the host team to equalize and the match ended 1-0 in favour of the north east. Speaking after presenting the trophy to the winning team, The Controller Nigeria Immigration service Kaduna State command, Bashir Muhammad Lawal expressed Delight with the performance of the entire...

Dan wasan Flying Eagles Haliru Sarki ya Sanya hannu Da kungiyar Al Ain.

Image
Dan wasan tawagar Flying Eagles ta najeriya Haliru Sarki ya sanya hannu akan kwantiragi da kungiyar kwallon kafa ta Al Ain dake yankin larabawa. Wannan kuwa na zuwa ne bayan da dan wasan ya nuna bajinta a gasa r cin kofin duniya na yan kasa da shekaru 20 da aka kammala a kasar Argentina. Da take tabbatar da sanya hannun kungiyarsa, Mahanaim FC tace tuni suka cimma yarjejeniya dan wasan Haliru Sarki da kungiyar da Al Ain kan daukarsa. Haliru Sarki, na daya daga cikin yan wasan najeriya da suka taimakawa najeriya ta samun zuwa mataki na gaba a gasar bayan zura kwallaye inda daga bisa Sukai rashin Nasara a hannun Korea. Usman Ibrahim