MAL-MOH zai tsaya takaran Shugaban Matasan APC a Shiyyar Arewa maso Yamma
1 Janairun, 2026 Daga Usman Ibrahim Mahuta A daidai lokacin da ake tunkarar babban taron Jam'iyyar APC na Kasa, Matasa daga Shiyyar Arewa maso Yamma na ci gaba da bayyana ra'ayin su na tsayawa takara a matakai daban daban. Na kwana kwanannan shine, Muhammad Abubakar Mal-moh Wanda ya bayyana aniyarsa na tsayawa takaran Shugaban Matasa na Jam'iyyar APC a Shiyyar Arewa maso Yamma. Taron ya gudana ne Jihar Kaduna inda magoya bayan Muhammad Abubakar Mal-Moh suka taru domin shaida ayyana kudirinsa na tsayawa takarar Shugaban Matasan Jam’iyyar APC na shiyyar Arewa maso Yamma, gabanin babban taron kasa na jam’iyyar da ke tafe. Da yake bayyana kudirinsa, Muhammad Abubakar Mal-Moh ya ce shawarar da ya yanke ta biyo bayan tuntuba mai zurfi da ga manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a matakin jiha da na kasa, musamman matasa. Ya bayyana cewa Shirin MAL-MOH an kirkire shi ne domin tallafawa kokarin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani wajen kar...