Posts

Kaduna Polytechnic tayi cikakken bayani akan jinkirin Kiran dalibai da suka Kammala karatu zuwa aikin yiwa Kasa hidima.

Image
  Daga Auwal Ahmed Ibrahim, Goronyo. 31 ga Janairu 2026 Hukumar Gudanarwar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta tarayya dake Jihar Kaduna (Kadpoly) ta fitar da sanarwa domin amsa korafe-korafen da wasu daliban da suka kammala karatu ke yi game da jinkirin kiran su aikin bautar ƙasa ta NYSC. Hukumar ta bayyana cewa wannan jinkiri ba na Kadpoly kaɗai ba ne, illa ya shafi dukkan manyan makarantu a faɗin ƙasar nan, musamman waɗanda ke da yawan ɗaliban da suka kammala karatu, sakamakon yawan tantance bayanai da matakan da ake bi. A cikin Sanarwa ta Musamman da Magatakardar Kwalejin, Dr. Muhammad Tanimu, ya rubuta kuma ya sanyawa hannu, ya bayyana cewa manyan abubuwan da ke haddasa jinkirin sun haɗa da rashin yin daidaitaccen regularization da Hukumar Shirya jarabawar shiga manyan makarantu ta Ƙasa JAMB), kura-kurai ko rashin cika takardun da ake buƙata daga ɓangaren waɗanda suka kammala karatu, da kuma tsarin rukunnan dalibai wato batch da NYSC ke amfani da shi. Magatakardar ya ƙara da cewa an...

An bukaci Teloli su Rika Cika Alkawari gabanin Azumin Watan Ramadan.

Image
 Daga Usman Ibrahim Mahuta  5 ga Watan Fabarerun 2025 An bukaci Teloli su Rika Cika Alkawari gabanin Azumin Watan Ramadan. A dai dai lokacin da Watan Azumin Ramadan ke kara kawo jiki, an Bukaci Teloli da su Rika Cika Alkawari idan an basu Dinki don biyan bukatun Al'umma. Mai Girma wakilin Mahuta Alhaji Yahuza Ibrahim ne yayi Kiran a lokacin da yake jawabi Wajen yaye dalibai Hudu da Suka Kammala koyon Aikin Dinki a garin Mahuta dake Karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna. Alhaji Yahuza Ibrahim ya ce ta Hanyar Cika Alkawari ne Sana'arsu dama kimarsu da jarajarsu zai daukaka a idan duniya yayin kuma ya ja hankalin Masu Bada Dinki su Rika biyan Telolin Hakkokinsu. A nashi jawabin, Mai Girma Sarkin Yakin Mahuta Dr Jafaru Bello Dambazau Wanda ya Samu wakilcin Malam Hussaini Mustapha ya nuna farin Cikin sa bisa Wannan Nasara da aka Samu Yana Mai Shan Alwashin bata tasa Gudunmuwar Wajen Bunkasa Sana'oi. Da yake jawabi akan Muhinmancin Sana'oi a tsakanin Matasa, Daya daga Cikin S...

Wakilin Sarkin Zuru ya Bukaci Samar da Cibiyoyin koyon Sana'oi

Image
 Daga Usman Ibrahim Mahuta  3 ga Watan Fabarerun 2025. An bukaci a samar da Karin Cibiyoyin koyon Sana'oi a Cikin Al'umma. Mai Girma wakilin Sarkin Zuru na Jihar Kaduna, Engineer Zubairu Kabir Danjuma ya bukaci Shugabannin da Sauran Masu Hannu da shuni su samar da Cibiyoyin koyon Sana'oi ga Matasa domin rage yawan zaman kashe Wando  Cikin Al'umma. Engineer Zubairu Kabir Danjuma ya bukaci hakan ne a lokacin da yake jawabi Wajen yaye dalibai Hudu da Suka Kammala koyon Aikin Dinki a garin Mahuta dake Karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna Wanda kungiyar Teloli na Mahuta ta shirya . Mai Girma wakilin Sarkin Zuru, ya bayyana Cewa matukar aka samar da Wuraren koyon Sana'oi zai taimaka ba kadanba domin kuwa Mata da Matasa zasu Samu aikinyi. Engineer Zubairu Kabir ya kuma shawarci Matasa da su kaucewa jiran Aikin Gwamnati a maimakon haka su Rungumi Sana'oin hannu domin shine kadai Hanya mafita Wanda zai su rike kansu. Ya Kuma jinjinawa kungiyar Teloli na Mahuta karkashin...

Northwell Academy ta Lashe Gasar W/ Sarkin Zuru December Cup U14 Mahuta sau biyu a Jere

Image
 25 ga Watan Janairun 2025 Daga Usman Ibrahim Mahuta. Kungiyar kwallon kafa ta Northwell Football Academy Makera dake Karamar hukumar Kaduna ta Kudu ta lashe Gasar December Cup Wanda Wakilin Sarkin Zuru na Jihar Kaduna Injiniya Zubairu Kabir Danjuma ya Shiryawa Matasa Yan Kasa da shekaru 14 a Mahuta. Northwell ta doke kungiyar kwallon kafa ta Lion Stars Football Club ne. da ci 3-2 a wasan karshe da Suka Buga a Asabar Dinnan kuma ya lashe Gasar sau biyu a jere kenan. Idan za a iya tunawa, a shekarar 2024 Northwell ce ta Doke Kungiyar kwallon kafa ta Athletic Academy a wasan karshe kuma ta Lashe Gasar. Dan wasan tsakiya Abdullatif Tajudeen shine ya lashe kyautar mafi kwazo a Kananan Yara sai Simon Friday ya lashe kyautar Wanda ya fi kowa Zura kwallo da guda hudu yayin da aka baiwa Daukacin kungiyoyin da Suka fafata a Gasar takardar Shaidar fafatawa a Gasar. Mai Girma wakilin Sarkin Zuru ya nuna Farin Cikin sa bisa irin Yan wasan Daya ganewa idanunsa Yana Mai jaddada muhinmancin wasan...

Golden Boys kawo ta Lashe Seyi Tinubu Kawo December Cup 2024 bayan Doke Tornadoes

Image
 13 Janairu, 2025 Daga Usman Ibrahim Mahuta  Kungiyar kwallon kafa ta Golden Boys Fc dake Kawo Kaduna ta lashe gasar cin kofin zaman lafiya wanda Seyi Tinubu ya dauki nauyi na Kawo December Cup bayan data doke Kawo Tornadoes da ci 4-2 a bugun daga kai sai mai tsaran raga a wasan karshen. Golden Boys ce ta fara zura kwallo jim kadan da fara wasan amma kafin aje hutun rabin lokacin Abdulazeez Butu na Kawo Tornadoes mai maida wasan 1-1 a a Zangon farko na wasan bayan da suka samu finareti inda daga nan ne aka je bugun daga kai sai mai tsaran raga. Yan wasan Tornadoes biyu sun barar da kwallo biyu wanda hakan ya baiwa Golden Boys lashe gasar. Da yake jawabi a lokacin wasan, Babban mai baiwa shugaban kasa Tinubu shawara akan hulda da al’umma a yankin arewa maso gabas,, Abdulhameed Yahaya Abba ya yabawa Seyi Tinubu da kwamitin shirya gasar bisa kokarin su inda ya kara da cewa sannu a hankali gasar na dawo da martabar kwallon kafa a jihar kaduna. Suma a jawabin su, shugaban karamar h...

Hon. Nasiru Ja’oji ya baiwa Golden Boys kawo Miliyan 5 bayan lashe gasar Seyi Tinubu kawo December Cup na 2024.

Image
  13 Janairu, 2025 Daga Usman Ibrahim Mahuta  A wani kokari na tallafawa bangaren wasanni a yankunan karkara, daya daga cikin shugabannin gudanarwa na kwalejin ilimi ta tarayya dake Potiskum a jihar Yobe, Mr Nasiru Bala ja'oji ya bada gudunmuwar kudi har naira miliyan biyar ga kungiyar kwallon kafa ta Golden Boys Fc dake Kawo a jihar kaduna. Mr Nasiru Ja’oji ya bada wannan gudunmuwa ne a lokacin da yake jawabi wajen wasan karshe na gasar December cup na kawo na 2024 wanda Seyi Tinubu ya dauki nauyi. Ya bayyana cewa gasar ya samar da dama ga yan wasan domin bayyana irin baiwar da ubangiji ya musu a bangaren wasan kwallon kafa yana mai cewa gwamnatin shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu a shirye take wajen tallafawa matasa a wannan bangare na wasanni. Bala Ja’oji ya kuma jinjinawa shugaban shirya gasar na Seyi Tinubu wato Musa Ibrahim bisa kokarin sa na hada kan al’ummar jihar kaduna inda ya bayyana shi a matsayin Babban nasara ga jama’a. Da yake jawabi akan irin tallafin da Seyi Tin...

TA TABBATA: Hukumar La Liga ta yiwa Dani Olmo da Pau Victor Rijista.

Image
 9 ga Watan Janairun 2025 Daga Usman Ibrahim Mahuta. TA TABBATA: Hukumar La Liga ta tabbatar da yiwa Yan wasan Barcelona Dani Olmo da Pau Victor Rijista. A ranar Laraba ne aka amincewa Barcelona ta yiwa Dani Olmo da Pau Victor Rijista kuma Sa'oi kadan hukumar La Liga ta tabbatar da Rijistan Idan Za a iya tunawa, Hukumonin La Liga da na kwallon kafa ta kasar Spaniya sukaita yin watsi tare da kin amincewa da yiwa Olmo da Victor rijista. Wannan Labari Mai Dadi ne ga yan Barcelona kuma a yanzu Yan wasan biyu, Olmo da Victor za su iya fafata wasan karshe na Spanish Super Cup tsakaninsu da Real Madrid a ranar Lahadi 12 ga watan Janairun 2025. Yan wasan biyu za su ci gaba da Buga Wasa har na tsawon Watanni uku Koda yake za a kara tsawaita lokacin bugawarsu har zuwa Karshen Wannan kakar Wasa idan Suka ci ga ba da yin Nasara a karar da Suka shigar.