Kaduna Polytechnic tayi cikakken bayani akan jinkirin Kiran dalibai da suka Kammala karatu zuwa aikin yiwa Kasa hidima.
Daga Auwal Ahmed Ibrahim, Goronyo. 31 ga Janairu 2026 Hukumar Gudanarwar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta tarayya dake Jihar Kaduna (Kadpoly) ta fitar da sanarwa domin amsa korafe-korafen da wasu daliban da suka kammala karatu ke yi game da jinkirin kiran su aikin bautar ƙasa ta NYSC. Hukumar ta bayyana cewa wannan jinkiri ba na Kadpoly kaɗai ba ne, illa ya shafi dukkan manyan makarantu a faɗin ƙasar nan, musamman waɗanda ke da yawan ɗaliban da suka kammala karatu, sakamakon yawan tantance bayanai da matakan da ake bi. A cikin Sanarwa ta Musamman da Magatakardar Kwalejin, Dr. Muhammad Tanimu, ya rubuta kuma ya sanyawa hannu, ya bayyana cewa manyan abubuwan da ke haddasa jinkirin sun haɗa da rashin yin daidaitaccen regularization da Hukumar Shirya jarabawar shiga manyan makarantu ta Ƙasa JAMB), kura-kurai ko rashin cika takardun da ake buƙata daga ɓangaren waɗanda suka kammala karatu, da kuma tsarin rukunnan dalibai wato batch da NYSC ke amfani da shi. Magatakardar ya ƙara da cewa an...