Posts

NPFL Mako na 24, Rangers ta doke Kano Pillars, Katsina United ta doke Abia Warriors

Image
  Sakamakon wasannin gasar Kwararru ta kasa bayan kammala wasannin mako na 24. 2 ga Janairun, 2026 Daga Usman Ibrahim. Sakamakon wasannin da aka buga mako na 24 na gasar kwararru ta kasa wato (NPFL) a ranar Lahadi a filaye daban-daban. Rangers International ta doke Kano Pillars da ci  2–0  sai Katsina United ma ta samu nasara akan Abia Warriors da ci  2–0  yayin da Bayelsa United ta sha kashi da ci  1–0  a hannun Enyimba. Sauran sakamakon wasannin sun nuna cewa Wikki Tourists da Nasarawa United sun tashi canjaras wato 1–1 sai kuma Niger Tornadoes ta yi canjaras 2–2 da Bendel Insurance. Haka kuma a Litinin dinnan za’a fafata sauran wasannin mako na 24 inda El-Kanemi Warriors za ta karɓi baƙuncin Kun Khalifat sai Barau FC Kano za ta fafata da Ikorodu City a Filin Wasa na tunawa da Marigayi Sani Abacha sai Kwara United za ta kara da Warri Wolves yayin da...

MAL-MOH zai tsaya takaran Shugaban Matasan APC a Shiyyar Arewa maso Yamma

Image
  1 Janairun, 2026 Daga Usman Ibrahim Mahuta  A daidai lokacin da ake tunkarar babban taron Jam'iyyar APC na Kasa, Matasa daga Shiyyar Arewa maso Yamma na ci gaba da bayyana ra'ayin su na tsayawa takara a matakai daban daban. Na kwana kwanannan shine, Muhammad Abubakar Mal-moh Wanda ya bayyana aniyarsa na tsayawa takaran Shugaban Matasa na Jam'iyyar APC a Shiyyar Arewa maso Yamma. Taron ya gudana ne Jihar Kaduna inda magoya bayan Muhammad Abubakar Mal-Moh suka  taru domin shaida ayyana kudirinsa na tsayawa takarar Shugaban Matasan Jam’iyyar APC na shiyyar Arewa maso Yamma, gabanin babban taron kasa na jam’iyyar da ke tafe. Da yake bayyana kudirinsa, Muhammad Abubakar Mal-Moh ya ce shawarar da ya yanke ta biyo bayan tuntuba mai zurfi da ga manyan masu ruwa da tsaki na jam’iyyar a matakin jiha da na kasa, musamman matasa. Ya bayyana cewa Shirin MAL-MOH an kirkire shi ne domin tallafawa kokarin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da Gwamnan Jihar Kaduna Sanata Uba Sani wajen kar...

MAL-MOH Unveils Ambition for APC North-West Youth Leader Seat

Image
Usman Ibrahim Mahuta  1 January, 2026  As preparations intensify ahead of the All Progressives Congress (APC) National Convention, youths across the North-West zone have continued to express interest in contesting for key leadership positions within the party. One of such aspirants is Muhammad Abubakar Mal-Moh, who has officially declared his intention to vie for the position of APC Zonal Youth Leader, North-West, under a project tagged “MAL-MOH Project.” Declaring his ambition, Muhammad Abubakar Mal-Moh said his decision followed wide consultations with key stakeholders of the party at both state and national levels, with particular emphasis on the youth. He explained that the MAL-MOH Project is designed to complement the efforts of President Bola Ahmed Tinubu and Kaduna State Governor, Senator Uba Sani in empowering young people, while also strengthening the APC’s grassroots support across the North-West zone. Speaking at the event, the Senior Special Assistant to the Kaduna...

Kaduna Polytechnic tayi cikakken bayani akan jinkirin Kiran dalibai da suka Kammala karatu zuwa aikin yiwa Kasa hidima.

Image
  Daga Auwal Ahmed Ibrahim, Goronyo. 31 ga Janairu 2026 Hukumar Gudanarwar Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta tarayya dake Jihar Kaduna (Kadpoly) ta fitar da sanarwa domin amsa korafe-korafen da wasu daliban da suka kammala karatu ke yi game da jinkirin kiran su aikin bautar ƙasa ta NYSC. Hukumar ta bayyana cewa wannan jinkiri ba na Kadpoly kaɗai ba ne, illa ya shafi dukkan manyan makarantu a faɗin ƙasar nan, musamman waɗanda ke da yawan ɗaliban da suka kammala karatu, sakamakon yawan tantance bayanai da matakan da ake bi. A cikin Sanarwa ta Musamman da Magatakardar Kwalejin, Dr. Muhammad Tanimu, ya rubuta kuma ya sanyawa hannu, ya bayyana cewa manyan abubuwan da ke haddasa jinkirin sun haɗa da rashin yin daidaitaccen regularization da Hukumar Shirya jarabawar shiga manyan makarantu ta Ƙasa JAMB), kura-kurai ko rashin cika takardun da ake buƙata daga ɓangaren waɗanda suka kammala karatu, da kuma tsarin rukunnan dalibai wato batch da NYSC ke amfani da shi. Magatakardar ya ƙara da cewa an...

An bukaci Teloli su Rika Cika Alkawari gabanin Azumin Watan Ramadan.

Image
 Daga Usman Ibrahim Mahuta  5 ga Watan Fabarerun 2025 An bukaci Teloli su Rika Cika Alkawari gabanin Azumin Watan Ramadan. A dai dai lokacin da Watan Azumin Ramadan ke kara kawo jiki, an Bukaci Teloli da su Rika Cika Alkawari idan an basu Dinki don biyan bukatun Al'umma. Mai Girma wakilin Mahuta Alhaji Yahuza Ibrahim ne yayi Kiran a lokacin da yake jawabi Wajen yaye dalibai Hudu da Suka Kammala koyon Aikin Dinki a garin Mahuta dake Karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna. Alhaji Yahuza Ibrahim ya ce ta Hanyar Cika Alkawari ne Sana'arsu dama kimarsu da jarajarsu zai daukaka a idan duniya yayin kuma ya ja hankalin Masu Bada Dinki su Rika biyan Telolin Hakkokinsu. A nashi jawabin, Mai Girma Sarkin Yakin Mahuta Dr Jafaru Bello Dambazau Wanda ya Samu wakilcin Malam Hussaini Mustapha ya nuna farin Cikin sa bisa Wannan Nasara da aka Samu Yana Mai Shan Alwashin bata tasa Gudunmuwar Wajen Bunkasa Sana'oi. Da yake jawabi akan Muhinmancin Sana'oi a tsakanin Matasa, Daya daga Cikin S...

Wakilin Sarkin Zuru ya Bukaci Samar da Cibiyoyin koyon Sana'oi

Image
 Daga Usman Ibrahim Mahuta  3 ga Watan Fabarerun 2025. An bukaci a samar da Karin Cibiyoyin koyon Sana'oi a Cikin Al'umma. Mai Girma wakilin Sarkin Zuru na Jihar Kaduna, Engineer Zubairu Kabir Danjuma ya bukaci Shugabannin da Sauran Masu Hannu da shuni su samar da Cibiyoyin koyon Sana'oi ga Matasa domin rage yawan zaman kashe Wando  Cikin Al'umma. Engineer Zubairu Kabir Danjuma ya bukaci hakan ne a lokacin da yake jawabi Wajen yaye dalibai Hudu da Suka Kammala koyon Aikin Dinki a garin Mahuta dake Karamar hukumar Igabi ta Jihar Kaduna Wanda kungiyar Teloli na Mahuta ta shirya . Mai Girma wakilin Sarkin Zuru, ya bayyana Cewa matukar aka samar da Wuraren koyon Sana'oi zai taimaka ba kadanba domin kuwa Mata da Matasa zasu Samu aikinyi. Engineer Zubairu Kabir ya kuma shawarci Matasa da su kaucewa jiran Aikin Gwamnati a maimakon haka su Rungumi Sana'oin hannu domin shine kadai Hanya mafita Wanda zai su rike kansu. Ya Kuma jinjinawa kungiyar Teloli na Mahuta karkashin...

Northwell Academy ta Lashe Gasar W/ Sarkin Zuru December Cup U14 Mahuta sau biyu a Jere

Image
 25 ga Watan Janairun 2025 Daga Usman Ibrahim Mahuta. Kungiyar kwallon kafa ta Northwell Football Academy Makera dake Karamar hukumar Kaduna ta Kudu ta lashe Gasar December Cup Wanda Wakilin Sarkin Zuru na Jihar Kaduna Injiniya Zubairu Kabir Danjuma ya Shiryawa Matasa Yan Kasa da shekaru 14 a Mahuta. Northwell ta doke kungiyar kwallon kafa ta Lion Stars Football Club ne. da ci 3-2 a wasan karshe da Suka Buga a Asabar Dinnan kuma ya lashe Gasar sau biyu a jere kenan. Idan za a iya tunawa, a shekarar 2024 Northwell ce ta Doke Kungiyar kwallon kafa ta Athletic Academy a wasan karshe kuma ta Lashe Gasar. Dan wasan tsakiya Abdullatif Tajudeen shine ya lashe kyautar mafi kwazo a Kananan Yara sai Simon Friday ya lashe kyautar Wanda ya fi kowa Zura kwallo da guda hudu yayin da aka baiwa Daukacin kungiyoyin da Suka fafata a Gasar takardar Shaidar fafatawa a Gasar. Mai Girma wakilin Sarkin Zuru ya nuna Farin Cikin sa bisa irin Yan wasan Daya ganewa idanunsa Yana Mai jaddada muhinmancin wasan...