Allah ya yiwa Sheik Shehu Usman Rigi-Rigi rasuwa
2 ga Janairu, 2026 Labari daga Abubakar Dan Yaro Innalillahi wainnailaihirrajiun: Allah ya yiwa Fitacccen Malamin Addinin Musulunci nan a Jihar Kaduna, Sheik Shehu Usman Idriss wanda aka fi Sani da Regi-regi na Manzon Allah. Kafin rasuwarsa Malamin ya shahara Wajen sanya mabiyansa da Sauran Al'ummar Musulmai nishadi Saboda salon wa'azinsa. Shiek Shehu Usman ya rasu ya bar Matansa 4 da yara 37 da jikoki da dama Za'a gudanar da Jana'izarsa da Karfe 4:30pm na yammacin yau idan Allah ya kaimu a Gidansa dake Kusfa Zaria. Da Fatan Allah ya gafarta Masa da Rahama Amin.